Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sanar da shirye-shiryen kafa masana’antu na cikin gida da cibiyoyin kasuwanci a wurare masu muhimmanci a fadin jihar domin hanzarta masana’antu, inganta samar da kayayyaki a gida da kuma samar da karin damammakin aikin yi.
Wannan na cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Juma’a.
Gwamna Yusuf ya bayyana hakan ne a lokacin taron raba tallafi ga mahautan da aka yi wa rajista, wanda Hukumar Sana’o’in Gida da Talla a Titi (CTSHA) ta shirya a Fadar Gwamnatin Kano.
Gwamnan ya ce an sanya wannan aikin a cikin kasafin kudi na 2026 da aka amince da shi, kuma manufarsa ita ce samar da cibiyoyin samar da kayayyaki na zamani ga masu sana’a da kananan ‘yan kasuwa.
Ya ce cibiyoyin za su samar da wuraren aiki da za a raba, kayan aiki na zamani, ayyukan samar da wuta da ruwa masu inganci, wuraren ajiya, ayyukan tallafin kasuwanci, horar da sana’a da kuma samun kasuwa mai tsari domin inganta yawan aiki da fafatawa.
Gwamnan ya ce wannan shiri ya yi daidai da Shirin Sabunta Fatarmu na Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta hanyar inganta kayayyakin da aka yi a Najeriya, tare da ci gaba da Shirin Kano A Farko na tallafa wa masu kasuwancin gida da bunkasa tattalin arziki.
Ya bayyana cewa cibiyoyin za su kuma hada da sassa na musamman ga mahauta, sarrafa nama, sarrafa fata domin karfafa hadin gwiwa da kayayyakin dabbobi da jawo karin zuba jari.
Gwamna Yusuf ya ce wannan shiri zai rage kudin samar da kayayyaki, inganta ingancin kayayyaki, fadada damar shiga kasuwa da kuma samar da dubban ayyukan yi ga matasa a bangarorin sarrafa nama, aikin fata, tattara kaya, sufuri, da sauran sana’o’i masu alaka.
Ya roki wadanda suka amfana da su sarrafa tallafin ta hanya mai kyau, su zama masu tsafta da sana’a ta gari, sannan su karfafa gwiwar saura don su yi rajista da hukumar domin su amfana da sauran shirye-shiryen gwamnati da ke tafe.














































