Dambarwar da ta faru a kwanan nan da ta shafi Dr. Nasa’i Gwadabe na Jami’ar Northwest da ke Kano ta sake jawo hankalin jama’a kan matsalar cin zarafin jima’i da ke ci gaba da samu a manyan makarantun ilimi a Najeriya.
Gwadabe, wanda malami ne na wucin gadi a Jami’ar Maryam Abacha (MAAUN) da aka danganta da zargin cewa ya nemi daliba da al’amurin jima’i, lamarin da ya janyo fushi a tsakanin al’umma bayan da aka ce mijin dalibar tare da wasu sun dake shi a wani bidiyo da ya bazu a shafukan sada zumunta.
Daga bisani, Jami’ar Maryam Abacha da aka ambata a cikin rahotannin, ta bayyana cewa aikin koyarwa na wucin gadi na Gwadabe a matsayin babban malami na tsawon shekara daya ya kare a watan Mayu 2026 kuma ba a sabunta shi ba.
Ko da yake ana bukatar yin bincike mai kyau da bin doka kan zargin da ake yi wa Gwadabe, amma tambayoyin da wannan lamari ya haifar ba su ta’allaka kan malami daya, daliba daya ko jami’a daya ba.
Suna da alaka da babbar matsala da ta dade a cikin tsarin ilimi mai zurfi a Najeriya tsawon shekaru. Sabon cece-kucen ya jawo hankali ba don kawai cin zarafin jima’i a manyan makarantu sabon abu ba ne, sai dai yana tunawa ‘yan Najeriya irin matsalar da ta zama alakakai a jami’o’i da kwalejoji a fadin kasar.
Akwai hujjoji da dama, wani rahoton Bankin Duniya na 2018 na aikin “Women, Business and the Law” ya nuna cewa kashi 70 na ‘yan mata masu digiri a Najeriya sun fuskanci cin zarafin jima’i a lokacin karatunsu, yawanci daga malami da abokan karatu.
Binciken baya bayan nan kuma ya nuna cewa sama da malami 50 a jami’o’i da kwalejojin gwamnati a Najeriya an zarge su da cin zarafi tsakanin Afrilu 2021 zuwa Afrilu 2025. Wasu an kori su, wasu an dakatar da su, yayin da wasu suka fuskanci hukunci.
Wannan kididdigar ta yi nuni da cewa ba za a iya cewa wata matsala ce ta wasu tsiraru. Maimaituwar samun irin wadannan matsalolin a manyan makarantu daban-daban na nuni da girman matsalar da ke da alaka da ikon malamai, alhakin makarantu da kuma kare dalibai.
Ga mazauna Jihar Kano, damuwa kan cin zarafin jima’i a manyan makarantu ba sabo ba ne. A 2019, an gurfanar da Ali Shehu, malamin wucin gadi a Kwalejin Kimiya da Fasaha ta Kano, a gaban kotun majistare kan zargin cin amana da cin zarafin jima’i da ya shafi wata daliba.
Kwalejin ta bayyana cewa Shehu ba ma’aikacin dindindin ba ne, amma sun kafa kwamitin ladabtarwa don gudanar da bincike kan lamarin.
A kwanan nan ma, wani bincike na 2025 a Jami’ar Bayero Kano ya nuna yadda matsalar cin zarafin jima’i ke ci gaba da kasancewa. Wasu ‘yan mata sun ce ba sa son yin magana a fili kan cin zarafin duk da cewa akwai doka, saboda tsoron sakamako.
Wannan binciken ya kuma duba zargin wata tsohuwar daliba kan wani malami a Jami’ar Bayero da ba a ambaci sunansa ba. Malamin ya musanta zargin kuma ya gabatar da sakonni, rikodin na murya da sauran takardu da ya ce suna nuna cewa zargin wani kokari ne na bata masa suna.
Wannan ya nuna wani bangare ta matsalar. Duk da cewa rashin daidaito kan ikon bangaren ka iya sa dalibai su kasance masu rauni, dole ne a gudanar da bincike kan zarge-zarge ba tare da son rai ba, kuma a yanke hukunci bisa hujja, ba bisa fushin jama’a ba.
Akwai kuma damuwar cewa a wasu lokuta dalibai kan fara tuntubar malamai ba bisa ka’ida ba ko neman fa’ida ta ilimi.
Wadannan halaye ba su ba da uzuri ga malamin da ya yi amfani da daliba ba. Sai dai suna kara nuna cewa malamai dole ne su kiyaye iyakar fanninsu ko da mecece dabi’ar daliba.
Idan muka bar Kano, ana ci gaba da samun irin wadannan matsalolin a makarantu a fadin kasar.
A Afrilu 2025, Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi ta kori Dr. Usman Aliyu, babban malami, bayan kwamitin ladabtarwa ya same shi da laifin cin zarafin wata dalibar mai suna Kamila Aliyu.
Dalibar ta zarge shi da tilastawa da barazana kan ci gaban karatunta. Wannan ya nuna daya daga cikin munanan bangarorin cin zarafi, yadda malamai ke da babban iko kan maki, kula da aiki da makomar daliba.
Kwanaki 10 kacal da suka wuce, Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Lagos ta kori malamai 3, Nurudeen Hassan, Kareem Arigbabu da Olayinka Uthman, bisa cin zarafi bayan da Majalisar Gudanarwa ta yanke hukunci.
A Nuwamba 2024, Jami’ar Tarayya da ke Lokoja ta kori malamai 4 kan cin zarafi.
A baya kuma, Jami’ar Ut Jihar Abia, ta dakatar da Dr. Udochukwu Ndukwe bisa zargi.
A Afrilu 2024, an kama Mfonobong Udoudom na Jami’ar Nigeria Nsukka bayan bidiyo ya danganta shi da cin zarafi, jami’ar ta dakatar da shi na dindindin.
A 2023, ICPC ta tuhumi Dr. Balogun Olaniran na Jami’ar Ilimi ta Tai Solarin bisa zargin neman jima’i da daliba domin canza sakamako.
A watan Maris, Kwalejin Kimiya da Fasaha ta Jihar Kogi ta kori Abutu Thompson bayan an zarge shi da zaluntar daliba.
A watan Agusta 2023, Jami’ar Calabar ta dakatar da Dean din tsangayar hari’a, Farfesa Cyril Ndifon, bisa zargin da wasu dalibai suka yi.
Jami’ar Lagos ma ta dakatar da Kadri Babalola a watan Satumba bayan zargin da ya shafi daliba mai shekaru 21.
A 2022, Jami’ar Abuja ta kori farfesoshi 2 kan cin zarafi, yayin da Obafemi Awolowo ta bude bincike kan wani farfesa. Shekara daya kafin haka, OAU ta kori malami 3 daga sashen Turanci, Dangantakar Kasa da Kasa da Lissafi.
Abin da ya fi damun kai shine al’adar yin shiru. Dalibai na guje wa rahotawa saboda tsoron ramuwa, kunya da rashin amincewa da tsarin. Wasu na tsoron a bayyana sunansu ko a ƙara cutar da karatunsu.
Sakamakon haka, yin shiru ya zama hanyar kare kai.
Saboda haka, samun doka kadai ba zai isa ba. Dokar da aka ajiye a cikin littafi ba ta kare daliba da bai amince da makaranta ba.
Matsalar ba wai rashin doka ba ne, galibi rashin aiwatar da dokar ne.
Najeriya ta yi kokari ta magance wannan matsala ta hanyar doka. A 2021, Majalisar Dattawa ta zartar da dokar da ta tanadi hukunci mai tsanani, har da dauri a kurkuku, ga masu cin zarafi.
Bayan shekaru, har yanzu dokar ba ta samar da cikakkiyar kariya da dalibai ba.
Dole ne Jami’o’i da kwalejoji su yi abin da ya wuce fitar da sanarwa lokacin da lamarin ya bazu. Dole ne su samar da muhimman hanyoyin bayar da rahoto wadanda ba za a san wanda ya bayar ba.
A bincika koke cikin gaggawa, kuma a fili da adalci. A kare dalibin da ya bayar da rahoto daga zalunci, yayin da ake bai wa wanda aka zarga damar kare kansa bisa doka.
Dole ne Malamai da ma’aikata a rika horar da su kan iyakar fannin koyarwa da dokokin cin zarafi. Dalibai a sanar da su hakkinsu ta hanyoyin bayar da rahoto.
Mafi mahimmanci, makarantu su nuna aikinsu cewa matsayi ko suna ba zai kare wanda ya ci zarafin daliba ba.











































