Kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint-Germain (PSG) ta ci gaba da rike kambunta a gasar cin kofin zakarun Turai ta UEFA a ranar Asabar bayan ta doke Arsenal da ci 4-3 a bugun daga kai sai mai tsaran-gida a wasan karshe mai cike da daure kai wanda aka tashi 1-1 bayan karin lokaci a birnin Budapest.
Kai Havertz ne ya fara sa Arsenal a gaba a minti na 6, amma bugun daga kai sai mai tsaran-gidan da Ousmane Dembele ya ci bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne ya baiwa PSG sabuwar dama, wacce daga karshe ta yi nasara a bugun daga kai sai mai tsaran-gida ta ci gaba da rike kofin Turai da ta lashe a bara.












































