Kotun Daukaka Kara Ta Kori Abba Gida-Gida A Matsayin Gwamnan Kano

Court of Appeal  750x430
Court of Appeal 750x430

A yau Juma’a ce Kotun Daukaka Kara take yanke hukunci kan tankiyar da ta dabaibaye zaben gwamnan Kano.

An dai gudanar da zaben ne tun a wata Maris, inda Hukumar Zabe ta Kasa INEC ta bayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya yi nasara.

Sai dai daga bisani jam’iyyar APC ta garzaya Kotun Sauraron Kararrakin Zabe, tana mai neman a sake nazari kan lamarin, inda ta samu nasara kotun ta ce dan takararta, Nasiru Yusuf Gawuna ya lashe zaben.

Kan haka ne NNPP ta garzaya Kotun Daukaka Kara tana mai neman hakki, inda bayan sauraron korafi da hujjojin kowane bangaren a makon jiya, ta ce za ta sanar da hukuncin a wannan Juma’ar.

Sai dai a zaman na wannan Juma’ar da ya gudana a Abuja, Kotun ta jaddada hukuncin Alkalan Kotun Sauraron Kararrakin da suka tabbatar cewa babu sunan Abba a rajistar ’ya’yan da Jam’iyyar NNPP ta bai wa Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), don haka bai cancanci tsayawa takara a karkashin inuwar jam’iyyar ba.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here