Kwankwaso Ya Sanar Da Gwarzo A Matsayin Dan Takarar Gwamnan NDC, Gawuna Ya Samu Tikitin Sanatan Kano Ta Tsakiya

IMG 20260529 WA0004 750x430

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Jagoran Sabuwar Jam’iyyar NDC, Rabiu Musa Kwankwaso, ya sanar da tsohon Mataimakin Gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo, a matsayin dan takarar gwamnan jam’iyyar a zaben 2027 a Jihar Kano.

Kwankwaso ya kuma bayyana tsohon Mataimakin Gwamna, Nasiru Yusuf Gawuna, a matsayin dan takarar Sanatan NDC a Kano ta Tsakiya.

Kwankwaso ya yi wannan sanarwar ne da safiyar ranar Juma’a a gidansa da ke Kano jim kadan bayan wani taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da magoya baya suka halarta.

Da yake jawabi a yayin taron, Kwankwaso ya ce NDC za ta bayyana ‘yan takarar sauran mukamai a duka matakai gabanin zaben 2027.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwa kan shirye-shiryen jam’iyyar da kuma hadin kai a tsakanin mambobinta, yana mai rokon su ci gaba da kasancewa tare da jajircewa wajen tabbatar da nasara a zabuka.

SolaceBase ta ruwaito cewa wannan ci gaba ana sa ran zai sake tsara yanayin siyasa a Jihar Kano yayin da manyan jam’iyyun siyasa ke kara karfafa shirye-shiryensu na zaben 2027.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here