Hukumar kula da gidajen yari ta musanta rahoton bullar tarin fuka a cibiyoyin tsare mutane

prisons

Hukumar kula da gidajen gyaran hali ta ƙasa NCoS ta musanta rahotannin da ke yawo cewa an samu bullar cutar tarin fuka tare da mutuwa a cibiyoyin tsare mutane, inda ta bayyana zarge-zargen a matsayin ƙarya da kuma karkatar da gaskiyar halin da kiwon lafiya ke ciki a wadannan cibiyoyi.

A wata sanarwa da aka fitar a Abuja, jami’ar hulɗa da jama’a ta hukumar, Jane Osuji, ta bayyana cewa ayyukan kiwon lafiya a dukkan cibiyoyin tsare mutane a faɗin ƙasa, ciki har da rigakafi da shawo kan tarin fuka, suna tafiya yadda ya kamata tare da tsari mai ƙarfi

Hukumar ta amince cewa wasu rahotanni da bincike masu zaman kansu sun nuna kalubale game da tarin fuka a gidajen yari a Nijeriya, amma ta jaddada cewa wajibi ne a duba irin wadannan bayanai cikin yanayinsu na gaskiya ba tare da yin babban hukunci mai ruɗani ba.

Osuji ta ce hukumar tana maraba da sahihin rahoton kafofin watsa labarai kan lafiyar jama’a da jin dadin wadanda ake tsare da su, amma ta ga dole ta mayar da martani kan labaran da ta kira masu jan hankali da kuma kuskuren fassarar gaskiya da ke cikin rahoton.

Ta bayyana cewa rahoton ya tuntubi hukumar kafin wallafawa domin neman bayani kan hanyoyin magani da matakan da ake dauka na rigakafi da dakile tarin fuka a cibiyoyin tsare mutane, inda aka ba shi cikakken bayani mai tushe da daidaito da manufofin ƙasa da ƙa’idojin kiwon lafiya na duniya.

Hukumar ta jaddada cewa tarin fuka matsala ce ta kiwon lafiya a duniya baki ɗaya, wadda ke shafar al’umma masu zaman kansu da na tsare, kuma tana bukatar hadin gwiwa mai ma’ana ba tare da tada hankalin jama’a ko nuna cibiyoyin tsare a matsayin wuraren hatsari ba.

Osuji ta bayyana cewa martanin Nijeriya kan tarin fuka na gudana ne karkashin Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya ta hanyar shirin ƙasa na yaki da tarin fuka, kuturta da kumburin wuya, inda NCoS ke taka muhimmiyar rawa ta hanyar gwaji, ganowa da magani kyauta ga duk wanda aka gano da cutar.

Ta kara da cewa cibiyoyin tsare mutane suna da dakunan lafiya, tsarin tura marasa lafiya zuwa manyan asibitoci idan bukata ta taso, tare da kokarin rage cunkoso da daukar karin ma’aikatan lafiya

Ta kuma tabbatar da kudurin hukumar na kare lafiya, mutunci da hakkin bil’adama na dukkan mutanen da ke tsare.

NAN

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here