Gwamnan Kano Zai Naɗa Kwamishinoni Daga Dala, Fagge, Nassarawa

gwamna, cututtuka, kula, amincewar, kafa, cibiyar
Majalisar dokokin jihar Kano ta samu takarda daga gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa neman majalisar ta duba tare da amincewa da bukatar kafa cibiyar yaki...

Gwamnan Kano,  Abba Kabir Yusuf ya miƙa wa Majalisar Dokokin jihar  takardar neman naɗa ƙarin kwamishinoni uku.

Kakakin Majalisar, Jibril Isma’il Falgore ne ya bayyana haka da safiyar Alhamis.

Ya ce mutanen da gwamnan ke neman naɗa wa un haɗa da Ibrahim Jibrin daga ƙaramar hukumar Fagge, Ibrahim Ali Namadi daga ƙaramar hukumar Dala, da Amina Abdullahi Sani daga ƙaramar hukumar Nassarawa.

Tun bayan da gwamnan ya miƙa sahun farko na jerin sunayen kwamishinoninsa ne ake samun ƙorafe-ƙorafe daga wasu ƙananan hukumomi da ba su samu wakilci a Majalisar Zartarwa ta jihar Kano ba.

Daga cikinsu akwai ƙananan hukumomin ƙwaryar birnin Kano da suka haɗa da Dala, Fagge, da Nassarawa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here