INEC ta ayyana Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Osun

Ademola Adeleke Accord Osun 750x430

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ayyana Gwamna mai ci kuma dan takarar Jam’iyyar Accord, Ademola Adeleke, a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Jihar Osun na 2026.

Jami’in INEC mai sanar da sakamako kuma Mataimakin Shugaban Jami’ar Tarayya ta Oye-Ekiti, Farfesa Joshua Olalekan Ogunwole, ne ya sanar da sakamakon a ranar Lahadi da safe bayan an kammala hada sakamakon daga kananan hukumomi 30 na jihar cikin dare.

A cewar Ogunwole, dan takarar Jam’iyyar Accord ya samu jimillar kuri’u 511,067 inda ya doke babban abokin hamayyarsa kuma dan takarar jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji, wanda ya samu kuri’u 444,815.

Babban Jami’in INEC mai sanar da sakamako ya ce Ademola Adeleke, da ya cika ka’idojin doka, an ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara kuma an mayar da shi zababbe.

“Anan nake ayyana cewa, Ademola Adeleke na Jam’iyyar Accord, da ya cika ka’idojin doka, an ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara kuma an mayar da shi zababbe, kamar yadda na sanya hannu,” in ji Farfesa Ogunwole.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here