A kowani lokacin zabe a Najeriya ana kawo irin wannan biki na yau da kullum, jam’iyyun siyasa da ‘yan takara suna taruwa a gaban shugabannin addini, manyan ‘yan siyasa, kungiyoyin jama’a da kafafen yada labarai suna gaisawa, yin jawabai kan zabe cikin lumana sannan su sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya ta kasa.
Sai kuma a kashe kyamarori, yakin neman zabe ya ci gaba, kalaman siyasa su kara tsanani, kuma a yawancin lokuta tashin hankali ya biyo baya.
Wannan na haifar da tambaya mai sauki amma mai tsauri:,mene ne amfanin ci gaba da sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya idan har tashin hankalin siyasa ya ci gaba kafin zabe, lokacin zabe da kuma bayan zabe?
Yarjejeniyar zaman lafiya ta kasa har yanzu tsari ne mai amfani, Najeriya na bukatar kowace hanya mai inganci da za ta hana tashin hankali a zabe, amma yarjejeniya da ba ta da sakamakon da za a iya gani ga masu karya ta da gangan na iya zama kawai “al’ada ta siyasa”.
An haifar da ita daga tarihi mai zafi
Tarihin Najeriya ya nuna cewa zabe ya kan haifar da tashin hankali da kashe-kashe.
An sanya hannu kan yarjejeniya a Abuja a ranar 14 ga Janairu 2015, tsakanin manyan ‘yan takarar shugaban kasa da shugabannin jam’iyyu kafin zaben 2015. Gidauniyar Kofi Annan ce ta goyi bayan wannan tsari domin hana tashin hankali a wani zabe mai zafi.
Kwanaki biyu kafin zaben shugaban kasa, a ranar 26 ga Maris 2015, Goodluck Jonathan da Muhammadu Buhari sun sake tabbatar da alkawarin su na zabe cikin lumana.
Daga nan aka samu Kwamitin Zaman Lafiya na Kasa karkashin jagorancin tsohon Shugaban Kasa Janar Abdulsalami Abubakar, wanda ke da manufarsa ta hada da karfafa kamfen cikin lumana, hana kalamai masu tayar da hankali da tashin hankali da kuma bukatar ‘yan takara su yarda da sakamako ko su bi hanyar shari’a idan suna da korafi.
Wannan tsari ya cancanci yabo saboda ya taimaka wajen samun sauya mulki cikin lumana a 2015 karo na farko tun 1999 da jam’iyyar da ke mulki ta mika mulki ga ‘yan adawa.
Amma nasarar 2015 bai kamata ta zama uzuri na mantawa da abin da ya biyo baya ba.
Tashin hankalin zabe ya wanzu kafin yarjejeniyar. A 2011, Human Rights Watch ta ruwaito cewa mutane sama da 800 ne aka kashe cikin kwanaki uku na tashin hankalin bayan zaben shugaban kasa a jihohi 12 na Arewa.
Wannan mummunan lamarin ne ya nuna dalilin da ya sa Najeriya ta bukaci tsarin da zai hana fafatawar siyasa ta rikide zuwa rikicin kabilanci da kisa.
To amma tambaya yanzu ita ce shin har yanzu yarjejeniyar na ba da kariyar da ‘yan Najeriya suka cancanta?
Yarjejeniyar bata dakatar da tashin hankali ba
A Disamban 2018, ‘yan takarar shugaban kasa da shugabannin jam’iyyu sun sake sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya ta kasa kafin zaben 2019. Yarjejeniyar ta bukace su da su yi kamfen bisa batutuwa da su nuna kin tayar da hankalin addini, kabila da yanki.
Amma duk da haka tashin hankali ya kasance babban al’amari a zaben 2019.
Human Rights Watch ta ruwaito cewa a Yuni 2019 mutane 626 ne suka rasa rayukansu a lokacin zaben, ciki har da masu kada kuri’a da jami’an zabe, inda ta danganta tashin hankalin ga ‘yan daban siyasa da kuma a wasu lokuta jami’an tsaro, tare da sukar rashin daukar mataki kan barazana da cin zarafi.
Kano ta kuma bayar da wani jan-kunne.
Gabanin zaben 2019, an ruwaito cewa rundunar ‘yan sandan Kano ta kama mutane 950 da ake zargin ‘yan daban siyasa ne cikin kwanaki tara, a cewar HumAngle, inda hakan ya nuna girman yadda ake shirya tashin hankali.
Shekaru hudu bayan haka, Kano ta sake shaida tashin hankalin zabe. A ranar 27 ga Fabrairu 2023, Channels Television ta ruwaito cewa an kone mutane har lahira bayan wasu ‘yan daba da ake zargi sun kai hari ofishin kamfen na NNPP a karamar hukumar Tudun Wada.
Wadannan abubuwan suna nuna cewa tashin hankalin zabe ba matsalar ranar zabe kadai ba ce, yana iya farawa tun lokacin yakin neman zabe, lokacin zabe, kuma ya ci gaba bayan an sanar da sakamako.
Barazanar 2026
Abin da ya faru a zaben gwamnan Osun na 2026 ya ba da wani misali mai cike da damuwa.
Jam’iyyu 14 da ke takara sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a ranar 30 ga Yuli 2026, a wani biki da kwamitin zaman lafiya na kasa ya shirya karkashin jagorancin Bishop Matthew Hassan Kukah.
Amma damuwa game da tashin hankali ta riga ta yi tsanani.
Wani bincike na Kimpact Development Initiative ya lissafa lamuran tashin hankali 73 masu alaka da zabe a Osun. Rahoton The Guardian da Premium Times ya ce mutane 29 ne suka mutu, yayin da ICIR ta ce 12.
CJID ma ta lissafa lamuran tashin hankali 34 da mutuwar mutane 18 a Osun tun daga watan Mayu 2026, ta kuma ruwaito cewa ‘yan sanda sun shaida kisan kai 30 da ke da alaka da siyasa a lokacin shirye-shiryen zabe.
Duk da bambancin lambobi, gaba daya suna nuni da barazana iri daya. Osun ta shiga zabe tana fama da tsananin damuwa kan tashin hankalin siyasa duk da akwai yarjejeniyar zaman lafiya.
Wannan ya kamata ya damu Najeriya.
Abin da aka rasa shi ne sauke nauyi
Nakasu mafi girma na al’adar yarjejeniyar zaman lafiya a Najeriya ba sanya hannu ba ne, rashin wata hanya da za a iya gani ta hukunta masu karya alkawari.
Yarjejeniyar zaman lafiya ba za ta iya maye gurbin tsarin shari’a ba, ba kuma za a iya ce wane mai laifi ne ba kawai saboda an ambaci sunansa.
Amma inda akwai ingantacciyar shaida da ta nuna cewa dan siyasa, dan jam’iyya, kungiyar yakin neman zabe ko magoya baya sun shirya, sun dauki nauyi, ko sun shiga tashin hankalin zabe, dole ne a bincika kuma a gurfanar da su gaban shari’a idan shaida ta isa.
Jam’iyyu ma su dauki nauyi.
Dan takara ba zai iya sanya hannu a bainar jama’a ya kuma bar magoya bayansa su yi tashin hankali a asirce ba, jam’iyyu su kasance da tsarin tarbiya ga mambobin da ke ingiza tashin hankali ko kalamai masu zafi.
Kwamitin Zaman Lafiya na Kasa da sauran masu ruwa da tsaki ma su wuce bikin sanya hannu.
Jama’a su san abin da ya biyo baya.
Wa ya karya alkawari?
Me aka bincika?
Me aka yi?
An hukunta jam’iyya?
An shigar da kara ga hukumomin tsaro?
Ba tare da amsoshin wadannan tambayoyin ba, yarjejeniyar za ta zama takarda da ‘yan siyasa ke sanyawa hannu domin babu tsadar siyasa wajen karya ta.
Najeriya na bukatar biki kadan
Manufar yarjejeniyar zaman lafiya ba daukar hoto ba ce, kariyar ‘yan kasa ce.
Ba za a yabi dan siyasa ba kawai saboda ya sanya hannu. Gwajin gaskiya yana farawa ne bayan biki.
Ya hana magoya bayansa?
Ya yi Allah-wadai da tashin hankalin da aka yi da sunansa?
Ya guji kalamai masu tayar da hankali?
Ya amince da sakamako na gaskiya?
Ya bukaci magoya bayansa su bi mataki na shari’a idan suna da korafi?
Ya ba da hadin kai wajen bincike?
Irin wadannan tambayoyin ne za su nuna ko yarjejeniyar tana aiki.
Najeriya ba ta bukatar a watsar da yarjejeniyar zaman lafiya, tana bukatar a karfafa ta.
Yarjejeniyar ta zama wani bangare na tsarin hukunci da ya hada jam’iyyu, hukumomin tsaro, INEC, kungiyoyin jama’a da shari’a.
A bibiyi zaman lafiya, a rubuta karya, a binciki zarge-zarge.
Mafi muhimmanci, ‘yan siyasa su fahimci cewa sanya hannu ba karshe ba ne. Farko ne.
Najeriya ba za ta iya ci gaba da shirya manyan bukukuwa ba inda ‘yan siyasa ke alkawarin zaman lafiya yayin da ‘yan kasa ke cikin tsoron tsoratarwa, rauni, kaura da mutuwa.
Kasar na bukatar ‘yan siyasa da suka fahimci cewa zabe fafatawa ce ta neman amincewar jama’a, ba yaki ba ne na neman karfi.
Sakon ya kamata ya kasance mai sauki:
Kada ka sanya hannu saboda yana da amfani a siyasa. Sanya hannu ne saboda kana da niyyar mutunta shi.
Kuma idan dan siyasa ko jam’iyya ba ta da niyyar hana tashin hankali, girmama ‘yan adawa ko amincewa da sakamako na gaskiya, to wani biki na sanya hannu ba zai canza komai ba.
Darajar yarjejeniyar zaman lafiya ta Najeriya ba za auna ta da adadin ‘yan siyasan da suka sanya hannu ba.
Za a auna ta da adadin ‘yan Najeriyar da za su iya jefa kuri’a ba tare da tsoro ba, su kuma su dawo gida lafiya.













































