Kungiyar City Boy, wani dandalin siyasa da wayar da kan jama’a daga matasa wanda ke mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Shirin Sabunta Fatan Al’umma baya, ta nada Kwamishinan Ma’aikatar Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi na Jihar Kano, Dr Dahiru Muhammad Hashim, a matsayin Mai Kula da Hulda da Wayar Da Kai na Yankin Arewa maso Yamma.
Jawabin nadin Hashim ya fito ne cikin wata sanarwa da Ofishin Mai Kula da Yankin Arewa maso Yamma na Kungiyar City Boy, Abdulazeez Abubakar Kaka ya fitar a matsayin wani mataki na karfafa tsarin jagoranci da wayar da kai na kungiyar a fadin yankin.
Kungiyar ta ce nadin Hashim ya nuna jajircewarsu na shigar da mutane masu kwarewa, gogewa da nasarori a cikin tsarin jagorancinsu yayin da suke kara fadada ayyukansu a jihohi bakwai na Arewa maso Yamma.
Hashim, likita ne, masani kan muhalli kuma ma’aikacin gwamnati, yana da gogewa a fannin muhalli, yaki da sauyin yanayi, hulda da jama’a da kuma gudanar da harkokin gwamnati.
A matsayinsa na Kwamishinan Ma’aikatar Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi na Jihar Kano, ya yi aiki a fannin ayyukan da suka shafi daidaita rayuwa da sauyin yanayi, dasa bishiyoyi, dawo da kasa zuwa asalinta da kuma sauya tsare-tsaren muhalli.
Sanarwar ta kuma nuna halartarsa manyan taruka na kasa da kasa kan yanayi, ciki har da Taron Majalisar Dinkin Duniya kan Sauyin Yanayi da Taron Afirka kan Yanayi.
Hashim shi ne wanda ya kafa Gidauniyar Panacea, wata gidauniya ta dasa bishiyoyi da kula da muhalli, gudunmawarsa wajen inganta muhalli ta samu karramawa a gida da wajen kasar nan, ciki har da ISTF Green Award ta shekarar 2025.
A cewar kungiyar, gogewarsa da tarihin aikin gwamnatinsa ya sanya shi kai wa matsayin da zai iya ba da gudunmawa mai ma’ana wajen wayar da kan jama’a da hulda da al’umma a fadin Arewa maso Yamma.
“Nadin sa yana nuna jajircewar Kungiyar na shigar da mutane masu kwarewa, gogewa da nasarori cikin tsarin jagorancinta yayin da take karfafa kasancewarta a fadin Arewa maso Yamma,” in ji sanarwar.
Kungiyar ta bayyana cewa tana da kwarin gwiwa cewa Hashim zai yi amfani da gogewarsa da alakar sa wajen tallafawa girma da ayyukan wayar da kai na kungiyar a fadin yankin.
“Muna taya Dr Dahiru Muhammad Hashim murna kan nadin sa kuma muna fatan zai bada gudunmawa mai amfani wajen wayar da kan jama’a ga Kungiyar City Boy a jihohi bakwai na Arewa maso Yamma,” in ji sanarwar.
Kungiyar City Boy ta ci gaba da fadada tsarin ta a Arewa maso Yamma cikin watannin baya-bayan nan, inda nadin-nadi ke nufin karfafa tsari, hulda da jama’a da kuma wayar da kai a yankin.













































