Dan takarar Mataimakin Shugaban Kasa na Jam’iyyar NDC, Rabiu Kwankwaso, ya bukaci Sanata Abdul’aziz Yari da ya sake tunani kan shawararsa na rike mukamin Darakta Janar na Kwamitin Kamfen din Shugaban Kasa na Jam’iyyar APC a zaben 2027.
Kwankwaso ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, inda yace tsarin kwamitin kamfen din APC ya nuna wa ‘yan Najeriya cewa zaben 2027 gwagwarmaya ce tsakanin wadanda ke son gwamnatin yanzu ta ci gaba da kuma wadanda ke neman canjin gwamnati.
Ya ce kwamitin ya kunshi ‘yan siyasa da dama da suka tallafa, suka kare ko suka yi aiki a gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
A cewarsa, wannan lamari ya haifar da tambaya kan ko APC na samar wa ‘yan Najeriya sabuwar hanya, ko kuma suna son ci gaba da tsarin da ya ce ya haifar da tsananin wahala ga ‘yan kasa.
Kwankwaso ya ce: “Gaskiyar magana ita ce, ina ganin zaben 2027 a matsayin gwagwarmaya tsakanin talakawan Najeriya da aka zalunta da kuma wadanda suka amfana, suka kare kuma suke ci gaba da tsarin da ya haifar musu da wahala.”
Ya nuna damuwa kan hauhawar farashin abinci da sauran muhimman kayayyaki, rashin aikin yi, karancin dama ga matasan Najeriya, rashin tsaro da kuma matsalolin da manoma da ‘yan kasuwa ke fuskanta.
Ya kuma yi Allah-wadai da matsin da ake fama da shi a fannin ilimi, lafiya da sauran muhimman ayyukan gwamnati.
Jagoran NNPPn ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi amfani da zaben 2027 wajen kin ci gaba da zalunci da kuma neman gwamnati da zata daukar nauyi da aikin al’umma.
“Idan mutanen Osun sun iya yin haka, sauran sassan kasar nan ma za su iya,” in ji shi.
Kwankwaso ya roki Yari, tsohon Gwamnan Jihar Zamfara kuma fitaccen dan siyasa a Arewa Maso Yamma, da ya yi tunani sosai kan shawararsa na jagorantar kamfen din APC.
“Na roki dan’uwana, Sanata Abdul’aziz Yari, wanda ya amince ya rike mukamin Darakta-Janar na Kwamitin Kamfen din Shugaban Kasa na APC, da ya yi tunani sosai ya sake yin la’akari da karbar wannan nauyi,” in ji shi.
Ya ce Yari, ganin ya taba zama gwamnan Jihar Zamfara, ya kamata ya san illar rashin tsaro, talauci, rashin aikin yi, kaura daga muhallai da kuma lalata hanyoyin samun arziki a yankin da kasar baki daya.
Kwankwaso ya yi tambaya kan ko Yari zai iya, bisa lamirin sa, jagorantar kamfen da ke neman ci gaba da gwamnatin da har yanzu ‘yan Najeriya da yawa ke fuskantar irin wadannan matsaloli a karkashinta.
Haka kuma ya nuna damuwa kan rahoton cewa an saka Shugaban Zartarwa na Hukumar Tara Haraji ta Najeriya, Dr Zacch Adedeji, da Darakta-Janar na Ofishin Kula da Kudi na Tarayya, Dr Tanimu Yakubu Kurfi, a cikin tsarin tara kudi da kudi na kamfen din.
A cewarsa, jagorancin muhimman hukumomin gwamnati na bukatar lura, amana da kuma amincewar jama’a.
Saboda haka ya kira ga Gwamnatin Tarayya da APC da su bayyana yadda shigar da manyan jami’an gwamnati masu alhakin tara kudin gwamnati da harkokin kudi na kasa a cikin tsarin siyasa na kamfen din ya yi daidai da amincewar jama’a.
Duk da haka Kwankwaso ya ce ikon karshe yana hannun ‘yan Najeriya ne.
“A karshe dai, babu wani kwamitin kamfen da ya fi karfin ‘yan Najeriya,” in ji shi.













































