Zaben Osun: INEC ta dora sama da kashi 25 na sakamako a tashar IReV

images 2026 07 06T164543.9761

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta dora sama da kashi 25 na sakamakon zaben gwamnan Jihar Osun a rambunta na Duba Sakamako IReV portal.

An fara dora sakamakon ne jim kadan bayan an kammala jefa kuri’a a rumfunan zabe da dama a fadin jihar, bayan karewar lokacin jefa kuri’a.

INEC ta ce karfe 2:30 na rana ce aka tsara a matsayin lokacin rufe zaben.

Zuwa lokacin da ake hada wannan rahoto, daga cikin rumfunan zabe 3,763 da ke jihar, an dora sakamakon rumfuna 1,011 a tashar IReV, wanda ya kai kashi 26.87 na jimillar sakamakon da ake sa ran.

Wannan ci gaba yana nuna fara watsa sakamako ta yanar gizo da kuma ba da damar jama’a su duba sakamakon rumfunan zabe yayin da jami’ai ke ci gaba da hada sakamakon zaben.

Tashar IReV tana baiwa jama’a da sauran masu ruwa da tsaki damar duba sakamakon da aka dora daga rumfunan zabe, wanda ke kawo karin gaskiya da rikon amana a tsarin zabe.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here