Babbar Alkaliyar Jihar Kano, Mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta sake nazarin shari’o’in mutane 82 da ke jiran shari’a (ATPs) yayin wani aikin duba gidajen gyaran hali da aka gudanar a jihar.
Jami’in Hulda da Jama’a na Hukumar Gyaran Hali ta Kasa (NCS), Shiyyar Jihar Kano, CSC Musbahu Lawan, ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a ranar Jumma’a, inda ya bayyana cewa an gudanar da aikin ne domin inganta sauri wajen gudanar da shari’a da kuma kare hakkokin mutanen da ke tsare.
A cewar sanarwar, an gudanar da aikin ne a gidajen gyaran hali na Kurmawa da na Goron Dutse, inda Babbar Alkaliyar ta duba shari’o’in da suka shafi fursunonin da suka shafe shekaru da dama a tsare ba tare da an gurfanar da su a gaban kotu a hukumance ba.
Yayin aikin, Aboki ta ba da umarnin sakin fursunoni bakwai nan take saboda dalilai na lafiya bayan la’akari da yanayin lafiyarsu da sauran yanayi da suka shafi ci gaba da tsare su.
Alkaliyar, yayin da take jawabi ga fursunonin, ta jaddada bukatar gudanar da shari’a cikin adalci da kuma jinkiri marar amfani.
Hukumar NCS ta ce wannan aikin ya nuna irin sadaukarwar da ma’aikatar shari’a ta jihar Kano ke yi wajen tabbatar da bin doka da oda, kare hakkin dan adam da kuma tabbatar da cewa ba a tsare mutane fiye da abin da doka ta amince da shi ba.
SolaceBase ta rawaiton cewa, Shugaban Hukumar Gyaran Hali na Jihar Kano, Ahmed Yusuf Lakpene, ya bukaci fursunonin da aka saka su dauki ’yancinsu a matsayin wata dama ta bude sabon shafi a rayuwarsu da kuma ci gaba da kasancewa masu bin doka.
Lakpene ya shawarce su da su guji ayyukan da za su iya janyo musu sabani da doka, sannan su yi amfani da damar da aka ba su ta hanya mai kyau.
Haka kuma ya jinjinawa Shugaban Hukumar Gyaran Hali na Kasa, CGC Sylvester Ndidi Nwakuche, mni, MFR, saboda samar da kyakkyawan yanayi na jiyya ga fursunoni a fadin gidajen gyaran hali.
Shugaban Hukumar Gyaran Hali na jihar Kano ya bayyana cewa, ayyukan duba gidajen gyaran halin na daya daga cikin kokarin da ake yi na rage cinkoso a gidajen gyaran hali da kuma tabbatar da cewa shari’a ta kasance mai sauki ga dukkan fursunoni.
Babbar Alkaliyar ta sami rakiyar Babban Rajistaran Babbar Kotun, Daraktan Shigar da Kara na Gwamnati (DPP), wakilan Kwamishinan ’Yan sanda, Masu Ba da Agajin Shari’a (Legal Aid Counsel) da sauran masu ruwa da tsaki a fannin gudanar da shari’ar manyan laifuka.
Hukumar NCS shiyyar Jihar Kano ta sake jaddada aniyarta na yin aiki tare da ma’aikatar shari’a da sauran masu ruwa da tsaki a fannin shari’a domin inganta shari’a cikin lokaci, rage cinkoso a gidajen gyaran hali da kuma kare hakkin mutanen da ke tsare.













































