An kori yan jaridu da lauyoyi daga zauren kotun dake gudanar da shara’ar Tukur Mamu a Abuja

0
Tukur Mamu 1 1 750x430

A ranar juma’an nan ne ya yin da babbar kotun gwamnatin tarayya da take gudanar da shara’ar Tukur Mamu a Abuja, ta umarci yan jaridu da lauyoyi da su fita daga cikin Kotun.

“Ina rokun wannan kotun mai albarka data bada umarni duk wanda wannan shara’ar bata shafe shi ba ya fita daga cikin kotun nan.”

Mai shara’ar ya karbe rokun da lauyan ya yi, inda ya umarci duk wani lauya wanda bada shi ake shara’ar ba ko kuma yan jaridu da duk wanda shara’ar bata shafe shi ba da ya fice daga zauren kotun.

Tukur Mamu dai na fuskantar shara’ar da gwamnatin taryya ke zargin sa da hada hannu da yan ta’adda a kasar nan.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here