Faransa Ta Kammala Janye Sojojin ta Daga Sansanin Sojin Kasar Chadi

Screenshot 2025 01 11 at 10 750x430

Kashi na karshe na sojojin Faransa a ranar Asabar sun tashi daga sansanin Abéché, sansanin soji na biyu a Chadi.

Kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rahoton cewa, an yi mika sansanin ne a wani bikin da ministan tsaro Issaka Malloua Djamouss ya halarta.

Ficewar sojojin da adadinsu ya kai 100 ya kawo karshen zaman sojojin Faransa a kasar da ke tsakiyar Afirka.
Dakarun Faransa sun kasance a kasar Chadi tun bayan da kasar ta samu ‘yancin kai a shekara ta 1960, inda suke ba da horon soji da kuma tallafin jiragen yaki da ‘yan tawaye.

Dakarun sun fara ficewa daga kasar Chadi a watan Disamba, tare da wa’adin janyewa gaba daya a ranar 31 ga watan Janairu bayan da kasar ta yanke shawarar kawo karshen hadin gwiwar soji da Faransa, tsohon mai mulkin mallaka.

A watan Disamba ne aka mika sansanin Faya ga gwamnatin Chadi bayan janye wani ayarin sojoji 120.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here