Dan Kwankwaso ya zama dan takarar mataimakin gwamna na NDC a Kano

Mustapha Rabiu Kwankwaso

Jam’iyyar NDC ta sanar da Mustapha Rabiu Kwankwaso a matsayin dan takarar mataimakin gwamnan Jihar Kano gabanin zaben gama gari na shekarar 2027 mai zuwa.

Sanarwar ta biyo bayan wani taron manyan masu ruwa da tsaki da aka gudanar a gidan jagoran kungiyar Kwankwasiyya na Kasa kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso da ke Miller Road a Kano.

SolaceBase ta ruwaito cewa Mustapha, wanda da ne ga tsohon gwamnan, zai zama abokin takarar dan takarar gwamnan jam’iyyar, Aminu Abdussalam Gwarzo, wanda shugabancin jam’iyyar ya zaba a baya a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar a zaben gwamna na 2027.

Kafin samun wannan takara, Mustapha Rabiu Kwankwaso ya taba zama Kwamishinan Matasa da Wasanni a Jihar Kano, inda ya samu yabo kan jagorantar shirye-shirye da dama na raya matasa da wasanni a lokacin mukamin nasa.

Ana sa ran NDC za ta kaddamar da cikakken tsarin kamfen dinta kuma ta fara tattaunawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyya a fadin jihar domin shirye-shiryen zaben gwamna na 2027.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here