Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Kano ta mayar da Muhammadu Sanusi II Sarkin Kano

kano, gwamnati, rushe, masarautu, sanusi
Gwamnatin Kano ta mayar da Muhammadu Sanusi II Sarkin Kano. Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ne ya sanar da hakan a wani taron maneman labarai da...
Daga: Sunusi A. Dantalata Fagge

Gwamnatin Kano ta mayar da Muhammadu Sanusi II Sarkin Kano.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ne ya sanar da hakan a wani taron maneman labarai da ya yi a fadar gwamnatiN jihar.

Gwamnan ya kuma bayar da umarnin cewa sarakunan da aka sauke su kwashe kayansu daga gidajen sarauta a cikin sa’o’i 48.

Karin labari: Da Dumi-Dumi: Majalisar dokokin Kano ta amince rushe sabbin Masarautu

Idan ba’a manta ba SolaceBase ta rawaito Majalisar dokokin jihar Kano da amince da dokar soke masarautunKano bayan kammala karatu na uku.
Dokar ta soke kafa sabbin masarautu guda 5 a jihar.
Kazalika duk ofisoshin da aka kafa a karkashin dokar da aka soke an kebe su da sabon kudirin.

Haka kuma duk hakimai da aka daukaka ko aka nada a karkashin dokar da aka soke za su koma kan mukamansu na baya.

Karin labari: Yanzu-yanzu: Majalisar wakilan Najeriya ta amince da kudirin komawa tsohuwar wakar kasa

Shugaban masu rinjaye kuma memba mai wakiltar mazabar Dala, Lawan Hussaini Chediyar Yan Gurasa ne ya dauki nauyin majalisar dokokin jihar Kano kan (gyara mai lamba 2) ta 2024.
Dokar wadda ta kafa sabbin masarautu guda biyar ta kasance tsohon gwamna Abdullahi Umar Ganduje ne ya fara sanya hannu a kan dokar a ranar 5 ga watan Disamba, 2019.

Gwamnan ya amince da gyara dokar a ranar 14 ga Oktoba, 2020 tare da sanya hannu kan wani gyara a ranar 11 ga Afrilu, 2023.

Sashi na 3 (1) na dokar ya kafa masarautu daban-daban guda biyar da suka hada da Kano, Bichi, Rano, Gaya da Karaye, tare da Karaye suna da ƙananan hukumomi takwas kowacce, yayin da masarautun Bichi da Gaya suke da ƙananan hukumomi 9 kowannensu, Masarautar Rano tana da ikon mallakar fiye da ƙananan hukumomi 10 daga cikin 44 na kananan hukumomi a jihar.

Lokacin da aka tsige Sarki Muhammadu Sanusi, wanda ya jagoranci majalisar a ranar 9 ga Maris, 2020, an yi wa dokar gyaran fuska a karanta: “Akwai shugaban majalisar wanda zai zama sarkin Kano”.

Sashi na 12 ya tanadi cewa gwamna na iya sanya mukamin sarki a matsayi na daya, ko na biyu, ko na uku bisa amincewar majalisar dokoki.

Wani babban jami’in majalisar, wanda bai so a ambaci sunansa ba, ya ce “babu wani tanadi da zai hana majalisar yin gyara ga doka.”

Zuwa yanzu dai Sarki Muhammadu Sanusi II, shi ne sabon sarkin da aka nada a matsayin dawayya kan karagal mulkin sarautar Kano karo na biyu.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here