Zaben Fidda Gwanin APC: Barau ya zama dan takarar Sanatan Kano ta Arewa

FB IMG 1779140466997 750x430

An tabbatar da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, a matsayin dan takarar jam’iyyar APC a yankin Kano ta Arewa gabanin babban zaben 2027.

Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa (NAN), ya ruwaito cewa Sanatan ya zama dan takarar ne bayan an tabbatar, wadda aka gudanar a Bichi, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Bichi a ranar Litinin.

NAN ta kuma ruwaito cewa dubban mambobin jam’iyyar ta APC daga kananan hukumomi 13 na yankin da jami’ai daga hedikwatar APC ta kasa sun halarci taron.

NAN ta ƙara ruwaito cewa daidai karfe 14:20, shugaban Kwamitin Zaben Fidda Gwanin Sanatan Kano ta Arewa na APC, Shehu Isa Direba, ya kira mambobin jam’iyyar da su tabbatar da takarar Barau.

Taron baki daya ya amsa da “eh.”

Shugaban Kwamitin Zaben Fidda Gwanin ‘Yan Majalisar Tarayya na APC a Jihar Kano, Hon. Musa Yahaya, shima ya nemi amincewar mambobin jam’iyyar ga takarar Barau na zaben ‘Yan Majalisar Tarayya na 16 ga Janairu, kuma ya samu.

Shugaban tawagar sanya ido kan zaben ta INEC, Mista Abdulrahman Haruna, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka gudanar da zaben cikin lumana da tsari.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, wanda Mataimakinsa Murtala Garo ya wakilce shi, ya yaba da tsarin zaben sannan ya bayyana kwarin gwiwar cewa Kano ta Arewa za ta baiwa Shugaba Bola Tinubu, Yusuf, Barau da sauran ‘yan takar APC kuri’a da yawa a babban zaben 2027.

“Muna farin ciki, Kano ta Arewa tana hannun APC a kowane lokaci.”

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here