Babbar Kotun Tarayya dake Abuja a ranar Litinin ta dage yanke hukunci a shari’ar da hukumar EFCC ta shigar kan kwace kadarori 57 da ake zargin suna da alaka da tsohon Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Abubakar Malami SAN, har zuwa ranar 10 ga Yuli.
Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ya ruwaito ce a ranar 26 ga watan Mayu, Mai shari’a Joyce Abdulmalik ta taba sanya ranar yau don yanke hukuncin.
Mai shari’ar ta sanya wannan kwanan bayan da lauyan EFCC, Jibrin Okutepa SAN da lauyan Malami da sauran wadanda ake kara, Adedayo Adedeji SAN, suka gabatar da takardu da hujjojinsu na goyon baya da kuma adawa da shari’ar.
Kotun ta sanya shari’ar a matsayin ta 4 a cikin jerin shara’un ranar Litinin, amma ba ta ci gaba ba.
Ko da yake ba a bayar da wani dalili na canza ranar ba, wasu shara’u 3 ma a cikin jerin shara’u 13 da ke gaban kotun an ba su sabbin kwanaki.
NAN ya ruwaito cewa hukumar yaki da cin hancin ta bukaci a yi kwacen kadarorin gaba daya bisa zargin cewa ba ta halastacciyar hanya aka same su ba.
A ranar da aka dage shari’ar ta baya, Okutepa ya shaida wa kotun cewa an shigar da wannan bukata ne a watan Fabrairu, kuma tana da takardar rantsuwa ta sakin layi 47 da na nuni 46.
Lauyan, wanda ya ce bukatar ta kunshi “kunduna 3,” ya roki kotun ta amince da shi.
Dogaro da takardun, ya bukaci kotun ta yanke cewa Malami da sauran wadanda ake kara sun “kasa gabatar da dalilin da ya kamata” na nuna cewa “an samu kayayyakin ta halal.”
A martaninsa, Adedeji ya ce an shigar da wannan bukata ne a ranar 27 ga Fabrairu kuma tana da takardar rantsuwa ta sakin layi 109 da Malami da kansa ya dada rantsuwa.
Ya ce an shigar da takardar rantsuwar ne don nuna dalilin da yasa bai kamata a bayar da umarnin kwacen kadarorin gaba daya ba.
Adedeji ya bukaci kotun ba wai ta soke umarnin kwace na wucin gadi da aka bayar a baya ba, har ma ta yanke cewa wadanda ake kara sun nuna cewa “ba a saya da kudaden laifi ba.”
Ya yi kalubalen cewa EFCC ta dogara ne kawai da zargi wajen cewa an sayi kadarorin da kudaden laifi.
“Kotu tana hukunci ne bisa hujja, ba zargi ba,” in ji shi.
Ya roki kotun ta yi watsi da hujjar lauyan EFCC.












































