Bangaren G7 na jam’iyyar APC Kano sun yi kira ga magoya bayansa da su kwantar da hankalinsu domin kuwa suna yin duk mai yiwuwa ta hanyar doka domin kwatowa ‘ya’yan jam’iyyar hakkinsu.
A cikin wata sanarwa da masu ruwa da tsaki na bangaren G7 suka fitar a ranar Juma’a, G7 ta tabbatar wa masu biyayya da magoya bayanta cewa za a kalubalanci hukuncin kotun daukaka kara a kotun koli saboda rashin gamsuwa da sakamakon da aka samu a kotun daukaka kara.
Jaridar Solacebase ta ruwaito cewa a ranar Alhamis ne kotun daukaka kara ta soke hukuncin da kotun babban birnin tarayya ta yanke wanda ta amince da zaben mazabu da bangaren Malam Ibrahim Shekarau suka gudanar, sabanin wanda bangaren Gwamna Abdullahi Ganduje ya jagoranta.
Sanarwar ta samu sa hannun Sanata Ibrahim Shekarau mai wakiltar Kano ta tsakiya, Sanata Barau I. Jibrin, Kano mai wakiltar Kano ta arewa, Tijjani Abdulkadir Jobe, dan majalisar tarayya mai wakiltar D/Tofa/Rimin Gado/Tofa, Nasiru Abduwa Gabasawa, dan majalisar tarayya mai wakiltar Gezawa, /Gabasawa, Barr. Haruna I. Dederi, dan majalisar tarayya mai wakiltar Karaye/Rogo, Sha’aban Sharada, dan majalisar tarayya mai wakiltar Kano Municipal da kuma Alhaji Shehu Dalhgatu, shugaban kungiyar Buhari Support Group.
Sanarwar ta ce: ”Hakika, muna girmama kotunanmu da tsarin shari’a sosai. Kuma kowane alkali yana da ikon da tsarin mulki ya ba shi damar yanke hukunci, ko ta wata hanya, dangane da duk wani lamari da ya zo gabansa.
”Duk da haka, tsarin ɗaukaka ƙararrakin Kotunan mu, yana ba wa wanda bai gamsu da hukuncin da wata Kotu ta yanke ba don ɗaukaka ƙara zuwa babbar kotu.”
“A kan haka ne muke kira ga dukkan magoya bayanmu a fadin jihar Kano da ma sauran sassan duniya baki daya da su kwantar da hankulansu domin kuwa lauyoyinmu sun fara shirin daukaka kara zuwa kotun kolin Najeriya, saboda rashin gamsuwa da hukuncin Kotun daukaka kara.”
”Muna kira ga magoya baya da su tsaya tsayin daka kan yin addu’o’in , kuma kada su bari wata magana ta rude su daga kowane bangare.”
Sanarwar ta ce, ”ku tuna cewa sau uku a jere muna samun irin wannan nasarori kuma a duk lokutan muna mika godiyarmu da godiya ga Allah Madaukakin Sarki ba tare da yin amfani da kalaman batanci ga kowa ba. Wannan shi ne girmamawa, abin da ko yaushe ake tsammani daga Shugabanni kenan.











































