Wani Kwamishinan Zamfara ya rasu a hatsarin mota

056F5CCA E57D 4215 AE15 EB6F36701958
056F5CCA E57D 4215 AE15 EB6F36701958

Alhaji Hashimu-Shehu Gazura, kwamishinan hukumar zabe mai zaman kanta ta Zamfara (ZASIEC), ya rasu.

Ya rasu ne a wani mummunan hatsari a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa Gazura kuma tsohon dan majalisar dokokin jihar Zamfara ne, mai wakiltar mazabar Gummi 2 .

Rasuwar tasa na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Shugaban Hukumar Majalisar dokokin jihar, Alhaji Mansur Bungudu ya fitar a Gusau ranar Asabar.

“Ya rasu ne a jiya (Juma’a) sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya afku a hanyar Yawuri a jihar Kebbi. Inji sanarwar.

“An shirya yin sallar jana’izar marigayin a fadar Sarkin Gummi ranar Asabar da karfe 11:00 na safe.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here