Likitocin masu Neman kwarewa da ke yajin aiki da kungiyar likitocin Najeriya (NMA) sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da gwamnatin tarayya kan yajin aikin da suka fara a ranar Laraba.
Da suke gudanar da sanya hannun, kungiyar likitocin tace, likitocin da ke yajin aikin sun shiga yajin aikin gargadi na kwanaki biyar ne domin tauna aya a bukatarsu na a inganta musu yanayin aiki.
Kakakin ma’aikatar kwadago da samar da ayyukan yi, Mista Olajide Oshundun, ya bayyana cewa an sanya hannu kan yarjejeniyar a ofishin ministan, Mista Chris Ngige.
“Wannan zama anyi shi ne da nufin dakatar da yajin aikin,” in ji shi.
Likitocin na kuma neman ayi musu kari kai tsaye a Tsarin Albashin su wanda zai kai kashi 200 cikin 100 na yawan albashin likitoci a halin yanzu.
Likitocin da ke yajin aikin sun kuma bukaci a sake duba Tsarin Albashin su wanda aka yi nazari a karshe a shekarar 2009 da kuma biyan bashin albashin da ba a biya ba na shekarar 2014 zuwa 2016.












































