Fursunoni Sama da Ɗari Biyu Sun Tsere a Jihar Kogi

images 2
images 2

Kimanin fursunoni 240 ne suka tsere daga Gidan Ajiya Da Gyaran Hali (MSCC) da ke Kabba a Jihar Kogi, bayan wani hari da har yanzu ba a san ko su waye suka kai ba.

Mai magana da yawun Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali Mista Francis Enobore ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa harin ya faru ne da tsakar dare ranar Lahadi.

Sanarwar ta ce maharan ɗauke da muggan makamai sun yi ba-ta kashi da masu gadin wajen.

Karanta Wannan: {BIDIYO}:Yadda Aka Ceto Ɗalibai 75 Da Aka yi Garkuwa Da Su A Zamfara

Sanarwar ta kara bayyana cewa Kwanturola – Janar, Haliru Nababa ya ba da umarnin a fara gudanar da bincike domin dawo da wadanda suka tsere nan take. ”

Kwanturola-Janar din ya kuma yi kira ga jama’a da su bai wa jami’an tsaro bayanan sirri da za su taimaka wajen kamo wadanda suka tsere, ” in ji sanarwar.

Karanta Wannan: Al’ajabi: Wani Dalibin Kwalejin Kimiyya Da Kere-Kere Ya Rataye Kansa

An kafa gidan gyaran hali na Kabba wato (MSCC) shekarar 2008 tare da damar dukar fursunoni 200.

Saidai a halin da ake ciki, fursunoni 294 na tsare daga cikin su 224 wadanda ake tsare da su gabanin shari’a da kuma fursunoni 70 da aka yankewa hukunci.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here