Dikko Radda ya nada shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa na jihar Katsina

Dikko Umar Radda 750x430
Dikko Umar Radda 750x430

Gwamnan jihar Katsina Umar Dikko Radda ya amince da nadin sabon shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar, da kuma Karin wasu nade-naden a fannoni daban-daban na jihar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran gwamnan, Malam Ibrahim Kaula ya rabawa manema labarai a Katsina ranar Laraba.

Kamfanin Dillancin Labarai na kasa NAN, ya rawaito cewa a kwanakin baya ne gwamnatin Radda ta kafa hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Katsina.

Sabbin wadanda aka nada sun hada da; Mai Shari’a Lawal Garba mai ritaya a matsayin sabon shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Katsina, sai kuma Alhaji Usman Mamman Maska a matsayin shugaban hukumar kula da kananan hukumomi.

An kuma nada mambobin hukumar yaki da cin hanci ta jihar da suka hada da Dakta Jamilu Abdussalam a matsayin babban sakataren hukumar, da Malam Usman Dalhatu da Malam Surajo Doro sai Alhaji Abba Mato da Alhaji Kabir Aliyu-Maska da Alhaji Nafiu Kuringafa da kuma Alhaji Bello Danmusa.

Dikko Radda ya kuma yi kira ga wadanda aka nada din da su daidaita tunaninsu yayi dai-dai da tsarin gwamnatinsa wajen ganin an samar da ci gaba mai dorewa ga mutanen jihar Katsina.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here