APC ta amince da Jamilu Gwamna a matsayin dan takarar gwamnan Gombe

IMG 20260503 WA03431 750x430

Jam’iyyar APC ta Jihar Gombe ta amince da Jamilu Ishiyaku Gwamna a matsayin dan takarar gwamna ta hanyar yarjejeniya a zaben shekarar 2027.

An sanar da wannan matakin ranar Lahadi, bayan wani babban taron masu ruwa da tsaki wanda Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, wanda shi ne jagoran jam’iyyar a jihar ya jagoranta.

Wata sanarwa da Darakta Janar a bangaren Yada Labarai na Gidan Gwamnati, Ismaila Uba Misilli, ya fitar ta ce taron ya cimma yarjejeniya baki daya na amincewa da Gwamna, tare da ‘yan takarar shawarwari da yarjejeniya na sauran mukaman zabe.

Masu ruwa da tsakin sun kuma tabbatar da ‘yan takara na Sanatoci uku na jihar, kujerun Majalisar Wakilai shida da duka mazabun Majalisar Dokokin Jiha 24, wanda ke nuna yadda aka yi amfani da tsarin shawarwari na bai daya sosai a fadin jihar.

Wata majiya daga jam’iyyar a taron ta ce matakin na nufin karfafa hadin kai da guje wa zaben fidda gwani mai rarraba kai gabanin babban zaben shekarar 2027.

“Tsarin yarjejeniya na yana nuna muradun gama gari da dabarun hadin kai a cikin jam’iyyar,” in ji majiyar.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here