Gwamnatin Tarayya ta janye takunkumin da ta sanyawa kamfanin Emirates

Emirates Airlines
Emirates Airlines

Gwamnatin tarayya ta dage takunkumin hana zirga-zirgar da ta sanyawa kamfanin jiragen sama na Emirates, a cewar ministan sufurin jiragen sama Hadi Sirika.

Idan za a iya tunawa, Najeriya ta dakatar da Emirates daga shawagi ko fita daga cikin kasarta bayan da kamfanin ya sanya wasu ƙa’idoji na gwajin COVID-19 ga fasinjoji daga Najeriya a cikin watan Maris.

Amma Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika ya sanar da dage takunkumin da aka sanya wa kamfanonin jiragen sama na Emirates a ranar Juma’a, a Abuja.

Yace “A yau mun sami tattaunawa da Emirates tare da cire wasu sharuɗɗan yin balaguron sabida iftila’in da ya ke faruwa”.

“Bayan hakan ya zama dole a dage haramcin da aka yi wa Emirates.

Wannan dage haramcin da ya biyo bayan samun matsaya daga tattaunawa tsakaninmu da su.” inji shi

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here