Gwamnatin Indiya ta sanar da haramta ayyukan wata fitacciyar kungiya da ke fafutukar tabbatar da ‘yanci Musulmi da masu alaka da ita tsawon shekara biyar.
Jami’ai a India na zargin kungiyar ta PFI da alaka da kungiyoyin masu ikirarin jihadi.
An bayyana PFI a matsayin kungiyar da ayyukanta suka saba dokoki.
A ranar Talata, ‘yan sanda sun kai samame ofisoshin kungiyar a jihohin kasar 7 tare da kama mutane sama da 100.
Magoya bayan kungiyar sun ce wannan dai wata bita da kullin gwamnatin BJP ta Hindu ce.













































