Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karrama fitattun ‘yan gwagwarmayar dimokuradiyya da masu fafutuka saboda gudummawar da suka bayar ga tsarin dimokuradiyyar Najeriya.
Daga cikin wadanda suka karbi lambobin yabo na kasa da aka sanar a bikin Ranar Dimokuradiyya na 2026 a ranar Juma’a akwai Sakataren Yada Labaran jam’iyyar NDC na kasa, Osa Director.
An lissafa Sakataren Yada Labaran NDC ne a cikin jerin ‘yan Najeriya kusan 50 da aka karrama saboda rawar da suka taka a gwagwarmayar tabbatar da dimokuradiyya wadda ta kai ga dawo da mulkin dimokuradiyya a kasar.
Yayin da yake sanar da lambobin a jawabin sa na Ranar Dimokuradiyya ga al’umma, Shugaba Tinubu ya ce wadanda aka karrama sun yi babbar sadaukarwa domin tabbatar da tseratar da mulkin dimokuradiyya a Najeriya.
A cewar Shugaban, da yawa daga cikin wadanda aka karrama sun sha azaba, dauri, gudun hijira, tsangwama, da sauran nau’ikan wahala yayin da suke yakin neman kawo karshen mulkin soja da kuma fafutukar samun mulkin dimokuradiyya.
Ya lura cewa sadaukarwarsu ce ta shimfida ginshikin ‘yancin dimokuradiyyar da ‘yan Najeriya ke morewa a yanzu.
Jerin wadanda aka karrama sun hada da ‘yan jarida, masu kare hakkin jama’a, shugabannin siyasa, da jami’an soja wadanda suka taka rawar gani a gwagwarmayar dimokuradiyya.
Tinubu ya ce an yi wannan karramawar ne domin karrama ‘yan Najeriyar da suka nuna jarumta da jajircewa wajen kare ka’idojin dimokuradiyya a wasu daga cikin lokutan siyasa mafiya wahala da kasar ta fuskanta.












































