SEDSAC ta yaba da nadin ‘yan gwagwarmayar kare hakkin dan Adam a matsayin kwamishinoni a Kano 

Abba Kabir Yusuf Kano 664x430

 

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta SEDSAC ta jinjina wa Gwamna Abba Kabir Yusuf kan nadin ‘yan gwagwarmayar kare hakkin bil’adama guda biyu a matsayin kwamishinoni a majalisar zartarwa ta Jihar Kano.

Cikin wata sanarwa da Daraktan SEDSAC, Comrade Umar Hamisu Kofar Na’isa, ya fitar a ranar Juma’a, ya bayyana nadin Ambasada Ibrahim Waiya da Comrade Nura Iro Ma’aji a matsayin abin yabo da nuna kyakkyawar fahimtar siyasa don ciyar da jihar gaba.

Sanarwar ta kara da cewa wadanda aka nada suna da tarihin aiki a fannin kare dimokuradiyya kuma suna da kishin kawo cigaba.

Kungiyar ta kuma bukaci su hada kai da kungiyoyin farar hula don habaka cigaban Kano.

A karshe, SEDSAC ta yi fatan Allah ya ba su ikon gudanar da ayyukansu don ciyar da jihar Kano gaba a fannin tattalin arziki da siyasa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here