Rundunar sojin saman Najeriya ta sanar da cewa ta cika dukkan alkawuran da ta dauka ga wadanda harin kuskure ya rutsa da su da iyalansu a ranar 11 ga watan Janairu a kauyen Dangebe da ke Maradun a jihar Zamfara.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na NAF, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar ranar Laraba a Abuja.
Ejodame ya kara da cewa, a baya babban hafsan sojin sama (CAS), Air Marshal Hasan Abubakar, ya aike da wata tawaga ta manyan hafsoshi domin gudanar da bincike, daga bisani kuma ya ziyarci Zamfara a ranar 6 ga watan Maris domin jaje.
Ya ce a yayin ziyarar, hukumar ta CAS ta gana da wadanda suka tsira da rayukansu, da iyalan wadanda suka rasa rayukansu, da kuma al’ummar yankin da abin ya shafa, inda suka yi alkawarin bayar da tallafi na gaggawa da kuma na dogon lokaci domin rage musu radadi.
Karin karatu: Yan sanda biyu sun jikkata, biyo bayan kashe ɗan ta’addar da ake nema ruwa a jallo a Kano
Ya kara da cewa wani alkawarin kuma shi ne gina rijiyar burtsatse a kauyen Kambarawa da ke kusa domin samar da ruwan sha ga al’ummar da ke kewaye.
Ya jaddada cewa shirye-shiryen wani bangare ne na dabarun hada karfi da karfe na NAF da nufin samar da hadin gwiwa da al’ummomin yankunan da rikici ya shafa.
“An kammala aikin sake gyaran gine-ginen da suka lalace, kuma an kai sabbin babura guda biyu.
“Bugu da kari kuma, an samu nasarar hakar rijiyar burtsatse da aka yi alkawarin samar da ruwa mai tsafta a kauyen Kambarawa da kewaye,” inji shi.
Ejodame ya kuma kara da cewa, an bayar da cikakken tallafin kudi da aka yi wa wadanda lamarin ya shafa da iyalansu alkawarin taimaka musu wajen farfado da rayuwarsu.
Ya ce iyalai da sauran al’ummar da lamarin ya shafa sun nuna matukar godiya ga hukumar ta NAF bisa ga gaskiya da tausayi da kuma cika alkawari cikin gaggawa.
Ejodame ya lura cewa shugabannin al’umma da mazauna yankin sun yaba wa NAF saboda ba wai kawai ta amince da wannan mummunan lamari ba amma saboda daukar kwararan matakai na samun waraka da tausayawa.
Ya kuma jaddada aniyar NAF na ci gaba da tabbatar da gaskiya da rikon amana a dukkan ayyukanta.(NAN)