A ranar Lahadin da ta gabata ne sabon gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya soke dukkan nade-naden mukamai da magabacinsa Gboyega Oyetola ya yi.
A jawabinsa na farko a ranar Lahadi Adeleke, tsohon dan majalisar dattawa, ya ce tsohon gwamnan ya dauki matakai da dama a kwanakin baya na mulki wadanda jihar ba tare da kudaden gudanarwa.
An bayar da kwangiloli daban-daba cikin gaggawa ga masu laifi ba tare da tanadin kasafin kuɗi ba.
Adeleke ya kuma ba umarnin garkame duk asusun gwamnati a bankuna da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi tareda gaggauta kafa kwamitin da zai gudanar da kididdiga da kwato dukkan kadarorin gwamnati.
Idan dai za a iya tunawa tsohon gwamnan jihar, Adegboyega Oyetola ya nada sakatarorin dindindin guda 30 kwanaki biyu kafin karewar wa’adinsa.













































