NLC ta yi barazanar mamaye ƙasar nan da Zanga-zanga sakamakon karin farashin wutar lantarki

NLC

Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC ta yi watsi da shirin gwamnatin tarayya na daidaita farashin wutar lantarki ga kwastomomin kamfanonin A, B da C.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi bayan taron majalisar zartarwa ta kasa a Yolan jihar Adamawa, kungiyar kwadago ta sha alwashin jagorantar zanga-zangar da za a yi a fadin Najeriya idan har gwamnati ta ci gaba da shirinta.

Karanta: TUC ta ki amincewa da karin kashi 65% na kudin wutar lantarki

A ranar Alhamis din da ta gabata, Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya ce za a daidaita farashin karami zuwa Band A.

A cikin sanarwar da ta fitar mai dauke da sa hannun Babban Sakataren NLC, Emmanuel Ugboaja, kungiyar kwadagon ta yi watsi da matakin.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here