NiMET ta yi hasashen samun hazo da hasken rana na kwanaki uku a Najeriya

Nigerian Meteorological Agency NiMET scaled 1 712x430

Hukumar kula da hasashen yanayi ta Najeriya NiMET ta yi hasashen samuwar hazo tare da hasken rana daga ranar Laraba zuwa Juma’a a dukkan sassan ƙasar.

Hasashen yanayin da hukumar ta fitar a ranar Talata ya nuna cewa za a samu yanayi mai ɗauke da hasken rana da hazo a tsawon kwanakin da aka ambata a Arewacin Kasar nan.

A cewar hukumar, yankunan arewacin ƙasar za su kasance cikin yanayin hasken rana tare da hazo a duk tsawon lokacin hasashen.

Hukumar ta yi hasashen cewa yankunan kudancin ƙasar za su samu sararin sama mai hasken rana tare da ɗan taruwar gajimare, kuma akwai yiwuwar samun tsawa a wurare kaɗan tare da ruwan sama mara yawa a wasu sassan jihohin Bayelsa, Rivers, Akwa Ibom da Cross River daga bisani a cikin rana.

Rahoton ya nuna cewa wannan yanayi zai ci gaba ba tare da wani babban sauyi ba a yankin arewa.

Hukumar ta bayyana cewa irin wannan yanayi na faruwa ne sakamakon sauyin yanayi da ke shafar iskar da ke yawo a sararin samaniya.

Ta ƙara da cewa jama’a su kasance masu lura da yanayin da ke gudana tare da ɗaukar matakan kariya da suka dace yayin wannan lokaci.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here