Majalisar wakilai ta dage zaman ta kan batun dokar gyaran haraji

download (1)

 

Majalisar Wakilai ta dakatar da zaman musamman da aka tsara yi don tattauna dokokin gyaran haraji da aka shirya gudanarwa a ranar Talata, 3 ga Disamba, 2024, har sai wani lokaci nan gaba.

Sakataren Majalisar, Dakta Yahaya Danzaria, ne ya sanar da hakan a wata takarda da aka raba wa ‘yan majalisar a ranar Asabar, wacce SolaceBase ta samu.

Tun da farko, Mataimakin Kakakin Majalisar, Benjamin Kalu, ya sanar da cewa za a yi zaman domin tattauna muhawara kan dokoki hudu na haraji da ke gaban Majalisar Tarayya.

Wadannan dokoki sun hada da Dokar Haraji ta Najeriya 2024, Dokar Gudanar da Haraji, Dokar Kafa Hukumar Haraji ta Najeriya, da Dokar Kafa Hukumar Hadin Gwiwar Haraji.

Sai dai, shugabannin Majalisar sun yanke shawarar dage zaman don bayar da damar yin karin tuntuba tare da dukkan masu ruwa da tsaki, ciki har da gwamnonin jihohi da wakilan yankuna, wadanda suka nuna adawa da dokokin da ake son kafa wa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here