Kwankwaso ya gana da Tinubu a birnin Paris

Tinubu 4 750x430 1
Tinubu 4 750x430 1

Shugaban kasa mai jiran gado, Bola Ahamad Tinubu ya gana da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda yana daya daga cikin wadan da suka fafata da Tinubu a zaben shuganan kasa da aka kammala a watan Fabarairun shekarar 2023.

Kwankwaso wanda yai takarar shugabancin kasa a jam’iyyar NNPP, ya ci jihar Kano ne kadai, inda ya kayar da jam’iyya mai mulki APC.

Majiyar mu ta bayyana mana cewa sun shafe awanni suna ganawa da junansu a ranar Litinin a paris babban birnin kasar Farance.

An rahoto cewa Tinubu ya nemi Kwankwaso da yaje yayi shawara da mashawartan sa akan bukatar a hada hannu tare domin su yi aiki tare.
Matar kwankwaso tare da zabben dan majalisar tarayya na jam’iyyar NNPP, Abdulmimin Jibrin, na daya daga cikin wadan da suka raka Kwankwso wajan taron, ya yin da kuma aka shiga taron da matar Tinubu da kuma shugaban majalisar wakilan Najeriya, Femi Gbajabiamila.

“Zababben shugaban kasar da kwankwaso sun shafe sa’a 4 suna ganawa a pari a ranar Litinin. An fara ganawar da misalin karfe 12: 30 har zuwa 4:45. Ganawar ta su ta sami halartar shugaban majalisar wakilan Najeriya, Inda Abdulmumin Jibrin ya raka kwankwaso.” Inji majiyar mu.

“Sen Oluremi Tinubu itama ta samu damar ganawa da matar kwankwaso hajiya salamatu, inda suka tau-tau na a kan tsohowar rayuwar su su ta baya tun lokacin da mazajan suna  majalisa a shekarar 1992, dakuma sauran hirar raki da suka shafi cigaban Najeriya, da kuma kokarin mijinta na gayyatar kwankwaso cikin gwamnatin sa, inda kuma kwankwason ya amsa gayyatar.

Mujiyr ta mu ta kara da cewa Tinubu na kokarin sasanta gwamna Ganduje da kwamskwaso.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here