Kotun Majistare ta ba da belin Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi

1684186122687
1684186122687

Kotun Majistare a Bauchi ta bayar da belin fitaccen malamin Musuluncin nan na jihar, Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi.

A ranar Talata ne kotun majistare ta 1 ta yanke hukunci a kan buƙatar beli da lauyoyin fitaccen malamin mai janyo ka-ce-na-ce, suka nema bayan an gurfanar da shi a gaban kotu.

A ranar Litinin ne, ‘yan sanda suka shigar da Sheikh Idris Dutsen Tanshi gaban babbar kotun majistare ta ɗaya, inda suka tuhume shi da tada hankulan jama’a.

Sai dai malamin ya musanta zargin.

Lauyoyinsa sun shaida wa kotu cewa laifin da ake zargin malamin da aikatawa ba zaii hana a bayar da shi beli ba, bisa tanadin dokokin Najeriya.

Daga nan sai alƙalin kotu ya sanya Talata a matsayin ranar da zai yanke hukunci game da buƙatarsu. Sannan ya ba da umarnin a ci gaba da tsare malamin a gidan yari kafin zaman kotu na gaba a washe gari.

Wata ƙungiyar addini mai suna Fityanul Islam ce ta kai ƙorafi kan malamin, tana zargin sa da furta miyagun kalamai a kan Annabi Muhammadu, sai dai Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi da magoya bayansa sun ce zargin ba gaskiya ba ne.

 

Barista Alƙassim Muhammad, ɗaya daga cikin lauyoyin Sheikh Idris Abdul’aziz ya shaida wa BBC cewa kotun ta bayar da belin malamin ne bisa wasu sharuɗɗa.

Ya ce sharaɗi na farko sai malamin ya gabatar da wani babban ma’aikacin gwamnati da ya kai matakin babban sakatare da kuma mai unguwa ko hakimi don su tsaya masa.

“Akwai kuma sharaɗin da za su gabatar da takarda, mallakan wani abu ko fili ko gida da ya kai naira miliyan biyar,” in ji Barista Alƙassim.

A cewarsa, kotu ta kuma buƙaci sai mutanen da za su tsaya wa Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi, su gabatar da hotunansu ga rijistaran kotu, kafin sakin malamin.

Tun da farko, rahotanni sun ce magoya bayan malamin sun cika harabar kotun ta Mai shari’a Abdulfatah Shekoni duk da ɗumbin jami’an tsaro da aka jibge waɗanda suka riƙa taƙaita shigi da ficen cincirindon mutane.

Barista Alƙassim Muhammad sai an cika dukkan sharuɗɗan belin ne kafin a saki Sheikh Idris Abdul’aziz.

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here