Iran ta nada Mukaddashin Jagoran Koli

Ayatollah Alireza Arafi

Iran ta nada mukaddashin Jagoran Koli bayan rasuwar Ayatollah Ali Khamenei sakamakon harin sama na hadin gwiwa tsakanin Amurka da Isra’ila a Tehran, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na IRNA ya ruwaito.

Babban malamin addini Ayatollah Alireza Arafi ne aka nada a matsayin mukaddashin Jagoran Koli na Iran.

Bisa kundin tsarin mulkin kasar, ya shiga cikin kwamitin shugabanci na wucin gadi da zai rika gudanar da ayyukan shugaban kasa har sai an zabi magaji.

Kwamitin ya kuma hada da Shugaban kasa Masoud Pezeshkian da Babban Alkalin kasa Gholam-Hossein Mohseni-Ejei.

Wannan hukuma ce za ta jagoranci kasar a lokacin mika mulki.

Sauye-sauye a rundunar IRGC

Hare-haren sun kuma yi sanadiyyar kashe manyan jagororin rundunar Islamic Revolutionary Guard Corps (IRGC). Rahotanni sun ce Babban Kwamandan rundunar, Janar Mohammad Pakpour, ya mutu.

An nada Ahmad Vahidi a matsayin sabon shugaban IRGC.

Rundunar na daga cikin manyan cibiyoyi masu karfi a Iran, tana kula da harkokin soja, siyasa da tattalin arziki, kuma tana aiki daban da rundunar soji ta kasa.

Hare-hare kan Iran

A ranar 28 ga Fabrairu ne aka fara farmakin hadin gwiwa tsakanin Amurka da Isra’ila kan gwamnatin Iran.

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce manufar yakin ita ce kawar da barazanar da Tehran ke haifarwa baki daya.

Sakamakon jerin hare-haren da aka kai, an kashe Jagoran Koli na Iran Ali Khamenei, ministan tsaro da kuma shugaban hafsoshin soji.

Iran ta mayar da martani ta hanyar harba makamai kan yankunan Isra’ila da sansanonin sojin Amurka a Bahrain, Kuwait da wasu kasashe makwabta.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here