Shugaba Muhammadu Buhari ya halarci taron bitan ayyukan ministoci karo na uku a fadarsa da ke Abuja yau Litinin.

Cikin wadanda suka samu halartan taron akwai tsohon shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta da mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo da shugaban majalisar dattawa Ahmed Lawan da kuma kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila.















































