Garo ya taya Ganduje murnar cika shekaru 75

Ganduje, Tinubu, APC, Kano, Gwamnati
Shugaban jam'iyyar APC na ƙasa wanda mazaɓarsa ta ce ta dakatar da shi, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin Jihar Kano ba ta isa ta ƙwace kujerarsa...

Alhaji Murtala Sule Garo, ɗan takarar mataimakin gwamna na jam’iyyar APC a zaben 2023 na jihar Kano, ya taya Dr. Abdullahi Umar Ganduje, shugaban APC na ƙasa, murnar cika shekaru 75.

Garo ya yi alfahari da shugabancin Ganduje, wanda ya kawo haɗin kai da kuma nasarar jam’iyyar APC a cikin zabe hudu daga cikinbbiyar.

Ya bayyana Ganduje a matsayin shugaban da ya nuna juriya, mayar da hankali, da hangen nesa.

Garo ya yi addu’ar samun lafiya, albarka, da nasara ga Ganduje a dukkan abubuwan da zai yi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here