Majalisar zartaswa ta tarayya ta amince da sake duba tare da inganta albashin ‘yan sanda da kashi 20 cikin 100.
Ministan harkokin ‘yan sanda, Maigari Dingyadi ne ya bayyana hakan a ranar Laraba bayan kammala taron majalisar zartarwa ta tarayya wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta.
A cewar ministan, ana sa ran sabon tsarin zai fara aiki daga watan Janairun 2022.
Dingyadi ya ci gaba da cewa, wannan lamarin ya biyo bayan bukatun da masu zanga-zangar EndSARS suka gabatar a shekarar 2020, wanda ya shafi inganta jin dadin jami’an ‘yan sanda.
Shugaba Buhari ya yi alkawarin cewa za a inganta albashin yadda ya kamata don ci gaba da wanzar da zaman lafiya a kasar.
FEC ta kuma amince da fitar da Naira biliyan 13.1 don biyan wasu alawus bayan mutuwar ma’aikata 5,472 da inshora daga 2013 zuwa Agusta 2021.












































