Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Mista Salihu Dembos a matsayin sabon shugaban gida talabijin na NTA.
Bayanin hakan na dauke cikin wata sanarwa da ministan yada labarai da al’adu Alhaji Lai Mohammed ya fitar yau Laraba a Abuja.
Sanarwar ta ce sabon shugaban zai yi aiki na tsawon shekaru uku ne a ofishin.
“Kafin nadin nasa, Mista Dembos ya kasance a matsayin shugaban sashin kasuwanci na gidan talabijin din NTA.” Inji sanawarwar.
“Mista Dembos ya shafe sama da shekaru 20 a matsayin gogaggen dan jarida.”
Sanarwar ta kara da cewa Dembos ya rike matsayin shugaban talabijin din ta NTA a Lokoja da kuma Kano.












































