Hukumar dake kula da tashi da saukar jirage ta kasa (FAAN) ta ce jami’an tsaro sun kama mutane uku da ake zargi da satar wayar wuta a filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Muhammed dake jihar Legas.
Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar ta FAAN, Abdullahi Yakubu-Funtua ya fitar ranar Juma’a.
Sanarwa ta ce an kama wadanda ake zargi ne a makarantar bada horo ta hukumar ranar Juma’a.
Sanarwa ta kara da cewa jami’an tsaro na hadin gwiwa ne suka yi nasarar kama wadanda ake zargin.













































