Ambaliyar ruwa: Kano na shirin samar da sabon tsarin magudanar ruwa – Mahukunta

Abba Kabir Yusuf Yusuf 750x430 (1)

Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar wa al’ummar jihar kan kudirin ta na magance matsalar ambaliyar ruwa a birane ta hanyar daukar matakan kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Kwamishinan Muhalli da Sauyin yanayi, Dakta Dahiru Hashim ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Kano, biyo bayan ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi a ranar Alhamis wanda ya yi sanadin ambaliya a sassan birnin.

Ya bayyana cewa mamakon ruwan sama da aka shafe sama da sa’o’i uku ana tafkawa a wurare da dama, ba a saba gani ba.

A cewarsa, hauhawar yanayin zafi a duniya ya kara danshin yanayi, wanda ya haifar da tsawaita da ruwan sama mai yawa wanda ya mamaye hanyoyin magudanar ruwa a babban birnin jihar.

Karin karatu: Gwamnatin Kano ta yi Allah wadai da korar ƴan Arewa daga Abuja

SolaceBase ta ruwaito cewa Dr. Hashim ya lura cewa matsalar ta kara tabarbarewa ne sakamakon saurin fadada birane, rashin isassun magudanar ruwa, da kuma toshe hanyoyin ruwa.

Kwamishinan ya tabbatar wa mazauna Kano cewa tuni gwamnati ta dauki matakai da dama domin dakile illolin ambaliya a birane.

Wadannan sun hada da yashe manyan magudanan ruwa a farkon damina, tallafawa kungiyoyin al’umma da kayayyakin aiki don gyara kananan magudanan ruwa, karfafa sarrafa sharar gida don hana toshewa, da maido da magudanan ruwa kamar bishiyoyin da ke kan manyan tituna.

Ya kuma bayyana cewa ana kan gina wata babbar tashar magudanar ruwa a magudanar Babangwari, wadda aka tsara domin isar da sama da rabin ruwan da ke cikin birnin.

Ya nanata kudirin ma’aikatar na kare rayuka da dukiyoyi a Kano daga ambaliyar ruwa da sauran hadurran da suka shafi yanayi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here