Gamayyar Kungiyoyin marawa Farouq Sule Garo sun saya masa fom din tsayawa takara domin cimma burinsa na zama Dan-Majalisar Wakilan Tarayya.
Kungiyoyin da suka hada da ‘yan mazabar sa da iyalai da abokan arziki sai kungiyoyin mata da abokan huldar kasuwanci a cikin gida Najeriya da ma kasashen ketare, sune suka tara sama da Naira miliyan 10 a karshen makon daya gabata domin siyan fom din.
Farouq, wanda ke da burin wakiltar mazabun Gwarzo da Kabo a Majalisar Tarayya, ya yi alkawarin ba zai ci amanar amincewar da aka yi masa ba matukar ya samu tikitin jam’iyyar, ya kuma yi nasara a babban zaben shekarar 2023.
“Ina mai matukar farin ciki tare da matukar mamaki, bisa wannan karramawa da mutane na suka min tare da nuna yardarsu da Kwarin gwiwarsu a kai na.” Inji Farouq.
‘’ Gudanar da managartan ayyuka ga al’ummar mu tare da daga darajar Yankin mu suna gaba cikin abubuwan da nake fatan gudanarwa idan lokaci ya yi.”











































