Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta dora sakamako 2,048 daga rumfunan zabe 2,445 a shafinta na kallon sakamako (IReV) har zuwa karfe 6:41 na yammacin ranar Asabar, wanda ke nufin kashi 83.7 na jimillar sakamakon zaben gwamnan Jihar Ekiti.
Wannan adadi ya nuna gagarumin ci gaba daga kashi 35.5 da aka dora kusan minti 30 da suka gabata da karfe 6:12 na yamma.
‘Yan takara goma sha hudu ne ke fafatawa a zaben gwamnan da ba na lokaci ba, inda Gwamna Biodun Oyebanji na Jam’iyyar APC ke neman wa’adi na biyu kafin wa’adin mulkinsa na farko ya kare a watan Oktoba.
Manyan abokan hamayyarsa sun hada da Oluwole Oluyede na Jam’iyyar PDP, Oluwadare Bejide na ADC, Oyebanji Olajuyin na LP, da Blessing Abegunde na NNPP. Sauran ‘yan takarar su ne Samuel Akande AAC, Ayodeji Ojo ADP, Opeyemi Felegan Accord, Joseph Anifowose APM, Bidemi Awogbemi APP, Olaniyi Ayodele PRP da Victor Adetunji ZLP.
Ana ci gaba da tura sakamako zuwa shafin yayin da ake ci gaba da tattara su a fadin jihar.











































