2027: APC a shirye take ta gudanar da zaben fidda gwani idan an kasa cimma yarjejeniya – Buni

Mai Mala Buni sabo

Gwamna Mai Mala Buni na Jihar Yobe ya ce jam’iyyar APC ta kuduri aniyar gudanar da zaben fidda gwani na adalci, gaskiya da gaskiya idan ba a samu ‘yan takar yarjejeniya ba.

Hakan na cikin wata sanarwa da Darakta Janar na Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Buni, Alhaji Mamman Mohammed, ya fitar a Damaturu a ranar Lahadi.

Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa (NAN) ya ruwaito cewa ‘yan takara shida na gwamna a jam’iyyar APC a jihar sun ki amincewa da dan takarar da jam’iyyar ta amince da shi, Alhaji Baba Wali, kuma sun nemi a gudanar da zaben fidda gwani na kai tsaye mai ciki da gaskiya.

‘Yan takar sune: Sanata Ibrahim Bomoi na Yobe ta Kudu, Alhaji Bashir Machina, Mista Kashim Musa-Tumsah, Mista Mustapha Maihaja, Alhaji Lawan Kolo da tsohon Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Mohammed Baba.

Buni ya ce jam’iyyar ba ta rufe kofar amfani da zabe kai tsaye wajen fitar da ‘yan takararta na mukaman da za a yi takara a zaben 2027 ba.

“Bayyana Baba Mallam Wali a matsayin dan takar da jam’iyyar ta fi so ya biyo bayan yanke shawarar da manyan masu ruwa da tsaki na ranar 23 ga Afrilun shekarar 2026.

“An amince da shi kuma aka karbe shi a matsayin dan takar da jam’iyyar ta fi so, amma idan babu yarjejeniya gabadaya, za mu bi hanyar zabe.

“Wannan ba sabon abu ba ne. A 2019, an zabe ni a matsayin dan takar yarjejeniya, wasu ‘yan takara kadan suka kalubalanci hakan, sai muka je zabe inda na samu nasara a matsayin dan takar jam’iyyar da rinjaye mai yawa, saboda haka muna shirye mu maimaita wannan tarihi idan ba za mu iya cimma yarjejeniya ba,” in ji shi.

Gwamnan dai ya ce jam’iyyar na ci gaba da tuntubar ‘yan takar da ke cikin damuwa da sauran masu ruwa da tsaki domin samar da sulhu cikin lumana ta hanyar tattaunawa.

“zan fi kowa zama cikin farin-ciki idan na ga jihar da jam’iyya na cikin lumana da hadin kai, mu har yanzu ‘yan asalin Jihar Yobe ne kuma mambobin APC. Abin da nake fatan gani shi ne mu kara hadi kai mu yi aiki tare domin ‘yan takararmu su yi nasara a zaben 2027.

“A matsayina na daya daga cikin wadanda suka kafa jam’iyyar APC, kuma tsohon Sakatare da Shugaban ta na Kasa, hadin kai da ci gaban jam’iyyar suna nufin komai a gare ni a matsayina na mutum. Zan ci gaba da goyon baya da kare manufofin jam’iyyar domin ta ci gaba da zama jam’iyyar da ke mulki a Najeriya,” in ji Buni.

Gwamnan ya bayyana kyakkyawan fata cewa burin duk ‘yan takara a jihar na neman mukaman gwamnati yana dogara ne kan son yi wa mutane hidima domin samun rayuwa mai kyau.

A cewarsa, Yobe ta zama misali na gaba wajen nuna gaskiya a siyasa, dimokuradiyya ta cikin gida da shiga kowa. Za mu ci gaba da rike wadannan ka’idoji domin habaka siyasa ba tare da kiyayya ba.

“Ina alfahari da cewa mu duka muna cikin wannan shawara tare da manyan masu ruwa da tsaki domin mu yarda da goyon bayan jam’iyyar a jihar, bayan duk haka, dukkanmu muna aiki ne domin alherin jihar.”

Buni ya ba da tabbacin cewa jam’iyyar za ta bai wa kowa matsayi, kuma za ta ci gaba da goyon bayan duk wanda ya fito a matsayin dan takararta domin APC ta yi nasara a zaben shugaban ƙakasa, gwamna da dukkan kujerun majalisar dokoki ta kasa da ta jihar.

“Ina kira ga duk mambobin APC a jihar da su rugumi hadin kai su kara samun goyon baya ga jam’iyyar domin ta ci gaba da zama jam’iyyar da ke mulki a Yobe da Najeriya domin baiwa Shugaba Bola Ahmed Tinubu nasara a jihar a wa’adinsa na biyu da duk sauran ‘yan takar APC,” in ji gwamnan. (NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here