YANZU-YANZU: Kotu ta ba da umarnin a kwace wasu kadarori da kudade masu alaka da tsohon gwamnan Zamfara

BREAKING 2
BREAKING 2

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a ranar Larabar ta ba da umarnin kwace wasu kadarori guda 10 da kudade a bankuna na wucin gadi da ake zargin tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari ne.

Alkalin kotun, Mai shari’a Obiora Egwuatu ya bayar da wannan umarni ne a lokacin da yake yanke hukunci kan karar da lauyan hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta ICPC Osuobeni Ekoi Akponimisingha ya shigar.

Mai shari’a Egwuatu ya ce umurnin na wucin gadi da aka bayar zai dauki tsawon kwanaki 60 domin baiwa ICPC damar kammala binciken da take yi, daga nan ne hukumar za ta iya neman a kwace mulki daga karshe.

Alkalin ya umurci ICPC da ta bayyana wannan umarni ga duk wani mutum ko masu sha’awar kadarorin da abin ya shafa su nuna dalilin da ya sa ba za a ba da su ga Gwamnatin Tarayya ba har abada.

A cewar ICPC, wasu daga cikin kadarorin suna Maryland (Amurka), Abuja, Kaduna da dai sauransu.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here