Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle ya aikewa majalisar dokokin jihar sunan Sanata Muhammad Hassan Nasiha a matsayin mataimakin gwamnan jihar.
A zama na biyu da majalisar ta yi a yau, kakakin majalisar, Nasiru Mua’zu, ya karanta wasikar da gwamna Bello Matawalle ya aiko wadda ta bayyana tsayar da Sanata Muhammad a matsayin mataimakin gwamnan jihar Zamfara.
Solacebase ta ruwaito cewa Wannan na zuwa ne sa’o’i bayan majalisar ta tsige Mahdi Gusau a ranar Laraba.
Sanata Hassan shine dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Zamfara ta tsakiya.












































