Hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta ta kasa ICPC, tace jami’anta dake sanya ido kan zaben gwamnan Jihar Osun, sun samu nasarar kama mutum 3 dake sayan kuri’u.
Mai magana da yawun hukumar Uwargida Azuka Ogugua, ce ta tabbatar da hakan ta cikin wata sanarwa da fitar ranar Asabar a birnin tarayya Abuja.
Tace guda cikin wadanda aka kama din mai suna Dapo Olayode, an kama shi ne a mazabar Iremo a yankin Ife ta Arewa, dake santoriyar Osun ta gabas.
A cewar sanarwar Olayode an kama shi ne da jerin sunayen masu kada kuri’a tare kuma da kwace waya a hannunsa kirar android.
Ta kara da cewa an kuma kama wanda ake zargi da siyan kuri’u da jerin sunayen mutane 100 da ake tsammanin za a biya kowannensu Naira dubu 5,000.
Ogugua, ta ce duk da rauni da shugaban masu sayan kuri’ar ya samu a kokarin guduwa, amma hukumar ta samu nasarar kwace littafin da ke dauke da jerin sunayen masu kada kuri’a su 100.













































