Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, ya shiga sabon jimami bayan rasuwar mahaifiyarsa, Hajiya Umma, wadda ta rasu a ranar Juma’a.
Rasuwar ta zo ne kwanaki kaɗan bayan ya rasa ‘yar uwar matarsa, Safiya Ali Rufai, wadda ta rasu a ranar 20 ga watan Maris na shekarar 2026 bayan gajeriyar rashin lafiya.
Ɗan El-Rufai, Bello El-Rufai, ya tabbatar da rasuwar a cikin wata sanarwa, inda ya bayyana lamarin a matsayin mai raɗaɗi ga daukacin iyalin.
Majiyoyi daga cikin iyali sun bayyana cewa marigayiyar ta dade tana fama da matsalolin lafiya da suka shafi tsufa, waɗanda suka tsananta a ‘yan kwanakin nan.
Haka kuma an nuna cewa lafiyarta ta kara tabarbarewa a daidai lokacin da ɗan mata yake fuskantar wasu sabbin al’amura da suka shafi hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta.
Kafin rasuwarta, an ruwaito cewa El-Rufai yana taka muhimmiyar rawa wajen kula da lafiyar mahaifiyarsa.
Iyalan sun yi addu’ar Allah ya gafarta mata kura-kuranta tare da ba ta aljannatul Firdaus.













































